1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Turkiyya : 'Yan adawa sun yi watsi da samakon zabe

April 20, 2017

Yayin da hukumar zaben Turkiyya ke tabbatar da amincinta kan zaben kasar na ranar Lahadi, jam'iyyun adawa sun lashi takobin kai batun babbar kotu don a bi musu kadi.

https://p.dw.com/p/2bZ2V
Türkei Proteste gegen Referendum in Istanbul
Hoto: picture alliance/dpa/AP/L. Pitarakis

Hukumar zaben kasar ta Turkiyya ta yi watsi da kiraye-kirayen jam'iyyun adawar kasar na a soke zaben raba gardamar fadada karfin ikon shugaban Raccep Tayyip Erdogan da aka yi a farkon wannan makon, zaben da aka yi zargin kura-kurai a cikinsa.Hakan dai ya haddasa zanga-zanga daga 'yan kasar wadanda suka yi kiran da a rusa majalisar jagororin hukumar zaben kasar, yayin da a daya hannun masu adawar ke tabbatar da cewar za su kai batun gaban babbar kotun kasar.