1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Turkiyya ta kai sabbin hare-hare a Idlib

March 2, 2020

Wasu hare-hare da Turkiyya ta kaddamar a Siriya, sun hallaka dakarun Shugaba Bashar al-Assad akalla 19 daidai lokacin da kasashen ke ci gaba da nuna wa juna yatsa.

https://p.dw.com/p/3YiL8
Syrien Idlib Offensive türkische Soldaten
Hoto: picture-alliance/AA/A. H. Hatib

Wani jirgin sama marar matuki ne dai ya kai harin kan jerin gwanon motocin sojin na Siriya a yankin Jabal al-Zawiya, kamar yadda kungiyar da ke sa ido kan yakin wato Syrian Observatory for Human Rights, mai cibiya a Birtaniya ta tabbatar.

Labarin ya kuma zo ne sa'o'i kalilan bayan kakkabo wasu jiragen yakin Siriya da Turkiyyar ta yi a yankin Idlib da ke arewacin Siriya.

Wannan dai yanki ne da Turkiyya ke goyon bayan mayakan da ke yi wa gwamnatin Siriya tawaye da ma kokarin kwace iko daga hannunta.

A makon jiya ne mayakan Siriya suka hallaka dakarun Turkiyya 34, abin da ya janyo martani daga Turkiyyar.