1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tsagaita bude wuta a Siriya

February 7, 2013

Shugaban Masar ya bayyana yiwuwar tsagaita bude wuta a Siriya nan bada jimawa ba.

https://p.dw.com/p/17aWq
Free Syrian Army fighters sit in trucks in Haresta neighbourhood of Damascus January 31, 2013. REUTERS/Goran Tomasevic (SYRIA - Tags: CONFLICT CIVIL UNREST POLITICS)
Hoto: Reuters

Shugaba Mohammed Morsi na kasar Masar ya bayyana fatan cewar nan bada dadewa ba za'a cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta a kasar Siriya, inda dubbanin jama'a suka rasa rayukansu, a rikicin kasar wanda dakarun gwamnati da kuma 'yan tawaye suka yi tsawon kimanin shekaru biyu suna gumurzu a tsakanin su. Shugaba Morsi, ya bayyana cewar, wani taron daya gudana a tsakanin kasashen Masar da Turkiyya da kuma Iran a gefen taron koli na kungiyar kasashen Musulmi a birnin alQahira na kasar Masar, ya tattauna matakan shawo kan rikicin na Siriya.

Shugaba Morsi ya shaidawa taron manema labarai na hadin gwiwa a tsakaninsa da takwarai aikinsa na Turkiyya Abdullah Gul cewar, abinda ke da muhimmanci a yanzu, shi ne kawo karshen zubar da jinin da ake yi a Siriya. Domin cimma wannan burin kuwa - a cewar shugaban na Masar, tilas ne sassan da ke cikin rikicin su cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta ba tare da wani lokaci ba, yarjejeniyar da kuma ya ce - da yardan Allah za a cimma nan kusa.

Dama dai taron kungiyar hada kan kasashen Musulmi na OIC ya bukaci warware rikicin na Siriya cikin ruwan sanyi kuma ta hanyar tattaunawa.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh

Edita        : Umaru Aliyu