Trump yace an kusa cimma yarjejeniya tsakanisa da Iran
May 23, 2026
A wata hira da ya yi da kafar yada labarai ta CBS, Trump ya ce yarjejeniyar za ta hana Iran mallakar makamin nukiliya, tare da tabbatar da cewa an dauki matakin da ya dace kan sinadarin uranium da Iran ta tace.
Trump ya ce ba zai sanya hannu kan wata yarjejeniya ba sai idan Amurka ta samu duk abin da take bukata.
Iran da Amurka tare da Pakistan da ke shiga tsakani sun ce an samu cigaba a tattaunawar da a ke yi domin kawo karshen rikicin.
A wata hira daban da ya yi da kafar yada labarai ta Axios, Trump ya ce zai tattauna da masu ba shi shawara kan sabon daftarin yarjejeniyar Iran, wanda zai tabbatar da yanke hukuncin ci gaba da yakin ko akasin haka.
Trump ya kuma gargadi Iran da cewa idan ba a cimma kyakkyawar yarjejeniya ba, zai dauki tsauraran matakai.