Transparency International ta baiyana rahotonta na shekara 2012
December 5, 2012A rahotonta na wannan shekara da ke shirin kammala da ta baiyana ,ƙungiyar Transparency International mai fafutukar yaƙi da cin hanci a duniya ,ta ce lamarin cin hancin da karɓar rashawa na ƙara zama babbar barazana ga ƙasashen duniya.
Kuma rahoton ya nuna cewar matsalar ta cin hanci ta shafi wasu ƙasashe na ƙungiyar Tarrayr Turai galibi masu fama da koma baya na tattalin arziki. Irin su Girka da Italiya waɗanda suka zo na 72 da kuma na 94 a jere a cikin sahun kasashe 170 da ƙungiyar ta gudanar da bincike.Ƙasashen Danmark da Finlade da Nuzilan sune ƙasheshen da suka fi rashin cin hancin a duniya
yayin da Somaliya da Koriya ta Kudu da Afganistan wanda ke a ƙarshe suka fi kowa cin hancin.
Mawallafi: Abdourahamane Hassane
Edita : Mohammed Nasir Awal