1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron Jeniva a kan batun nukiliya na Iran

November 8, 2013

Ministocin harkokin waje na ƙasashen Faransa da Jamus da Ingila sun isa Jeniva domin tattauna batun shirin nukliya na Iran tare da takwaransu na Amirka John Kerry.

https://p.dw.com/p/1AEDV
U.S. Secretary of State John Kerry speaks to the media after a meeting of the foreign ministers representing the permanent five member countries of the United Nations Security Council, including Germany, at the U.N. Headquarters in New York September 26, 2013. U.S. and Iranian officials emerged upbeat on Thursday from a meeting on Iran's nuclear program but both sides also sounded a cautionary note, with the United States saying there was more work to do and Iran insisting on quick sanctions relief. REUTERS/Eric Thayer (UNITED STATES - Tags: POLITICS)
Hoto: Reuters

Sakataran na harkokin wajen Amirka John Kerry ya katse ziyarar da yake a yankin Gabas ta Tsakiya domin halartar taron wanda babbar kantomar Ƙungiyar Tarrayar Turai kan manufofin ƙetare Catherine Asthon da kuma MDD ke jagoranta.

Ana sa ran a wannan ganawa ta manya ƙasashen duniyar guda biyar haɗe da Jamus,za a cimma wata yarjejeniya ta tarihi bayan da aka kwashe shekarun da dama shirin na gamuwa da cikas. A wani tayin sassantawa kan batun da ba bayyana ba yazuwa yanzu, Iran ta amince ta yi watsi da wani ɓangare na shirinta na nukiliya da kishi 20 cikin ɗari. To amma firaminstan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce babban kuskure ne mai tarihi kasashen duniyar zasu yi, idan suka amince da tayin na Iran.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Umaru Aliyu