1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tallafawa al'umma a kewayen tafkin Chadi

Salissou BoukariJuly 28, 2016

Babban jami'in da ke kula da ayyukan agaji na Majalisar Dinkin Duniya Stephen Obrien ya nemi da a agaza wa al'umma a wasu yankuna na Najeriya da Tafkin Chadi.

https://p.dw.com/p/1JXHY
Stephen OBrien PK UN
Stephen Obrien mai kula da fannin agajin gaggawa a Majalisar Dinkin DuniyaHoto: Getty Images/AFP/L.Beshara

A cewar babban jami'in na Majalisar Dinkin Duniya ma kula da agajin gaggawa, dubabban al'umma ne ke cikin mawuyacin hali amma kuma ana mantawa da su. Mista Obrien ya jaddada wannan kira ne a gaban Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, inda ya yi kira ga kasashe da sauran masu hannu da shuni da su bada tasu gudunmawa cikin gaggawa. A kalla dai mutane miliyan tara ne ke cikin bukatar agaji a wadannan yankuna na arewa maso gabashin Najeriya da kuma kewayen tafkin Chadi.