1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taliban sun kashe dan uwan ma'aikacin DW

Abdullahi Tanko Bala
August 20, 2021

Mayakan Taliban sun harbe daya daga cikin dangin wani dan jaridar tashar Deutsche Welle tare da yi wa wani dan uwansa mummunan rauni a lokacin da suka kaddamar da farmakin neman dan jaridar.

https://p.dw.com/p/3zI3n
Afghanistan | Taliban Kämpfer in Kabul
Hoto: Rahmat Gul/AP/picture alliance

 

Yan Taliban din dai sun dade suna neman dan Jaridar na tashar DW wanda a yanzu yake aiki daga nan Jamus. Sauran danginsa sun tsere inda a yanzu suke buya.

Shugaban tashar DW Peter Limbourg ya yi Allah wadai da harin inda ya yi kira ga gwamnatin tarayyar Jamus ta dauki mataki. Yace kisan da yan Taliban suka yi wa wani dangi na daya daga cikin editocin mu abin daga hankali ne kwarai wanda ya nuna irin halin da ma'aikatan mu da kuma iyalansu suke fuskanta a Afghanistan.

A halin da ake ciki 'yan Taliban din suna bi gida-gida suna farautar yan Jarida a Kabul da sauran gundumomi.