1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Takunkumi ga Sudan ta Kudu

Lateefa Mustapha Ja'afarSeptember 2, 2016

Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya isa Sudan ta Kudu da nufin yin barazanar sanya takunkumin hana sayar da makamai da ma na karya tattalin arziki ga mahukuntan kasar.

https://p.dw.com/p/1Jv6L
Shugaba kasar Sudan ta Kudu Salva Kiir
Shugaba kasar Sudan ta Kudu Salva KiirHoto: Getty Images/AFP/M. Sharma

Kwamitin ya ce in har gwamnati taki amincewa da kara tura dakarun wanzar da zaman lafiya na majalisar 4,000 zuwa kasar to tabbas za ta fuskanci takunkumi. Ziyarar ta Kwamitin Sulhun na Majalisar Dinkiin Duniyar dai, za ta mayar da hankali ne ga yunkurin majalisar na sake tura dakarun wanzar da zaman lafiya a Sudan ta Kudun domin kare rayukan fararen hula da ke fuskantar hare-hare da fyade daga dakarun gwamnati. Mahukuntan kasar ta Sudan ta Kudu dai sun bayyana wannan yunkuri na Majalisar ta Dinkin Dunyia da wani sabon nau'i na yi musu mulkin mallaka. Ana sa ran wakilan Kwamitin Sulhun na Majalisar Dinkin Duniya za su gana da Shugaba Salva Kiir na Sudan ta Kudun, da nufin tilastawa bangarori biyu da ke yakar juna a kasar komawa domin yin amfani da yarjejeniyar sulhu da aka cimma a shekarar da ta gabata ta 2015.