1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Scotland ta nuna tirjiya da zabin Birtaniya na fata daga EU

Suleiman Babayo June 25, 2016

Takaddama ta kunno kai inda yankin Scotland na Birtaniya zai kare matsayinsa a Tarayyar Turai bayan ficewar Birtaniya daga kungiyar.

https://p.dw.com/p/1JDZV
Schottland Nicola Sturgeon in Edinburgh
Babbar ministar yankin Scotland Nicola SturgeonHoto: picture alliance/Photoshot

Yankin Scotland na kasar Birtaniya ya bayyana cewa zai fara tattaunawa domin kare matsayinsa karkashin kungiyar Tarayyar Turai, bayan daukacin Birtaniya ta kada kuri'ar fita daga kungiyar. Jagorar yankin Nicola Sturgeon wadda ta kira taron gaggawa na majalisar zartaswar yankin ta ce za su duba duk hanyoyin ganin kare yankin a Tarayyar Turai.

Sturgeon ta kara da cewa ganin yadda daukacin mazabun da suke yankin aka zabi ci gaba da zama cikin Tarayyar Turai haka ya nuna za a sake kiran zaben raba gardama na zama ko kuma ficewar yankin daga cikin hadaddiyar kasar Birtaniya. Sannan ta ce tabbacin zama a Tarayyar Turai ya saka 'yan yankin suka zabi ci gaba da kasancewa a Birtaniya yayin zaben raba gardama na shekara ta 2014, kuma yanzu yanayin ya sauya, saboda Birtaniya za ta fice daga Tarayyar Turai.