Taba Ka Lashe: 09.11.2016
November 12, 2016Talla
A kwanakin baya ne masana ilmin waka da a turance ake cewa Poetry suka gudanar da wani taron kara wa juna sani na mako guda a tsakanin 'yan kasashen nahiyar Afirka a birnin Legas cibiyar kasuwanci a tarayyar Najeriya. Taron ya biyo bayan wani makamancinsa ne da cibiyar raya al'adun Jamus ta Goethe Institut a Legas ta shirya wa masana ilmin rubuce rubuce da wake musamman ga matasa domin zama masu dogaro da kai maimakon zaman kashe wando.