1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taƙaddama tsakanin China da Japan

December 13, 2012

Ƙasashen biyu na ci gaba da yin takun saƙa a kan tsibirin Senkaku wanda ko wane daga cikin ɓangarorin ke yin iƙirarin cewar mallakarsa ne

https://p.dw.com/p/171ly
©Kyodo/MAXPPP - 02/09/2012 ; NAHA, Japan - Photo taken from a Kyodo News helicopter shows Uotsuri Island, part of the Senkaku Islands in the East China Sea on Sept. 2, 2012. A Tokyo metropolitan government team the same day conducted an offshore inspection of the islands as part of its plan to buy land on the isles amid a growing territorial row with China over the uninhabited islets. (Kyodo)
Hoto: picture-alliance/dpa

Rikici tsakanin ƙasar China da Japan a kan tsibirin Senkaku, ya ƙara zafafa,bayan da Japan ta sanar da cewar wani jirgin sama bincikke na yaƙi na ƙasar ta China ya keta sararin samaniyarta a karon farkon tun da ricikin ya rincaɓe a cikin watan Satumbar da ya gabata,a lokacin da wani ɓangaran tsibirin ya zama mallakar Japan.

Kakkakin gamnatin ta Japon Osamu Fujimura ya ce sun aike da jiragen yaƙi guda fudu a sansani ,sai dai ya ce babu wata karawa da aka yi tsakanin jiragen na ƙasashen biyu.China ta buƙaci Japan da ta dai'na, gudanar da harkokin a cikin ruwayen da sararin samaniyar tsbirin na Diayou wanda ta ce mallakarta ne.Wannan al'amari ya faru ne a sa'ilin da ƙasar China ke gudanar da bukukuwan nuna juyayi na zagayowar cikkar shekaru 75 da aikata kisan kiasun da Japan ta yi a kan yan China a garin Nankin.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Halima Balaraba Abass