1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Firaministan Habasha ya ziyarci Sudan don yin sulhu

Abdoulaye Mamane Amadou
June 7, 2019

Shugaban gwamnatin Habasha Abiy Ahmed ya soma wata ganawa da bangarorin dabam-dabam a Sudan a wani mataki na shiga tsakani don kawo karshen zaman rashin tabbas da kasar ta ke ciki a yanzu.

https://p.dw.com/p/3K2yF
Äthiopien Sudan Premierminister Abiy Ahmed und General Abdel Fattah Al-Burhan Abdelrahman
Hoto: Reuters/M. N. Abdallah

Firaministan Habasha Abiy Ahmed ya sauka a wannan rana ta Juma'a a babban birnin Khartum na kasar Sudan, a wani yunkurin da yake na shiga tsakani don sasanta bangarorin da ke jayayya da juna na soja da fararen hula.

A ziyarar, Abiy Ahmed zai gana da majalisar mulkin sojan Sudan ta rikon kwarya, kana zai kuma yi wata tattauana wa da ‘yan fafatuka a daidai lokacin da daukacin kasashen duniya ke yin Allah wadarai da matakin sojan kasar na kisan masu bore da zanga-zanga.

Yanzu hakan dai manyan titunan babban birnin kasar Khartoum na ci gaba da kasancewa a kufai, kana kuma wasu sauran shagunan na ci gaba da zama a rufe, inda rahotanni suka ce sojoji ne kawai ake iya gani a ko ta ina.

Akalla mutane 113 ne wasu rahotanni ke cewa sojan sun hallaka, sakamakon kakkabe masu zanga-zangar da suka yi share wuri zauna a farkon wannan makon, lamarin da kuma ya kara janyowa majalisar sojan yankon jini.