1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Soma zaman makoki na kwanaki uku a Nijar

Salissou BoukariFebruary 19, 2015

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta fara bincike tare da ayyana zaman makoki na kwanaki uku daga Alhamis bayan da wasu jirage suka kai harin bama-bamai a garin Abadam.

https://p.dw.com/p/1EeMG
Hoto: DW/M.Kanta

A lokacin da yake magana kan wannan lamar,i kakakin gwamnatin ta Nijar kuma ministan shari'ar kasar Marou Amadou, ya ce za'a gudanar da bincike domin gano jirgi ko kuma jiragen da suka yi wannan danyan aiki.

An dai fara makoki na kwanaki uku a fadin kasar ta Nijar daga yau Alhamis domin tunawa da marigayan wadanda aka kashe yayin da suka taru kusa da wani masallaci sakamakon wani rishi da suka samu a wannan gari, inda harin ya yi sanadiyar rasuwar mutane a kalla 36 tare kuma da jikkata wasu a kalla 20. Sai dai tuni mazauna wannan gari suka tabbatar cewa jiragen na Najeriya ne. Ko ma dai minene bincike ne kawai zai tabbatar da hakan, saboda gwamnati ta ce za iya kokarin tabbatar da zahirin abin da ya faru.