1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Holland da Birtaniya sun soma zaben EU

Gazali Abdou Tasawa
May 23, 2019

Al'ummomin kasashen Holland da Birtaniya sun soma a wannan Alhamis gudanar da zaben 'yan majalisar dokokin Turai wanda za a kwashe kwanaki uku ana gudanar da shi daga wannan kasa zuwa waccan a cikin kasashe mambobin EU.

https://p.dw.com/p/3Ivva
Niederlanden EU-Wahlen
Hoto: picture-alliance/dpa/ANP/B. Maat

Mutane kimanin miliyan 400 masu rijistan zabe a kasashen 28 na Turai za su zabi 'yan majalisar dokokin Turai guda 751. An dai bude runfunan zaben ne tun da misalin karfe biyar da rabi agogon JMT a kasar ta Hollande mai kujeru 26 a majalisar Turan.

Alamu na nuni da cewa jam'iyyar FVD mai akidar adawa da Kungiyar Tarayyar Turai da kuma kyamar 'yan gudun hijira ta Thierry Baudet dan shekaru 36 ce za ta zo a matsayi na daya a zaben. 

A Birtaniya kuma mai shirye-shiryen ficewa daga Kungiyar ta EU  da kuma ke da kujeru 73 a cikin majalisar Turan an bude runfunan zaben ne a karfe shida agogon GMT.