1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojojin Kwango sun kwace gari mai mahimmanci

October 30, 2013

Dakarun gwamnatin Jamhuriyar Demokradiyyar Kwango na samun galaba kan 'yan tawayen gabashin kasar.

https://p.dw.com/p/1A9IZ
Hoto: Carl de Souza/AFP/Getty Images

Dakarun na gwamnatin Kwango dai sun kwace garin Bunagana na gabashin kasar daga hannun kungiyar 'yan tawaye ta M23. Kakakin gwamnatin kasar Lambert Mende, ya bayyana haka wa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP, inda ya ce an yi musanyan wuta tun da sanyin safiyar wannan Laraba, kafin fatattakar 'yan tawayen.

Kakakin gwamnati ya tabbatar da kwace garin da ke zama mafi girma a hannun 'yan tawayen, wanda ke kan iyaka da kasar Yuganda. Wani jami'in sojan Majalisar Dinkin Duniya ya gaskata labarin kwace garin na Bunagana da ke da nisan kilo-mita 80 a arewacin birnin Goma.

Majalisar Dinkin Duniya na zargin 'yan tawayen na M23 da aikata laifukan yaki cikin gabashin kasar ta Jamhuriyar Demokradiyyar Kwango.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Usman Shehu Usman