1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojojin Faransa sun kashe 'yan kishin Islama 60 a Mali

January 14, 2013

Tun daga ranar Juma'ar da ta gabata ne dai rundunar sama na kasar Faransa ke taimakawa wa dakarun Mali da ke yaki da yan kishin Islama da suka kwace iko da arewacin kasar tun watannin da suka gabata.

https://p.dw.com/p/17JY5
Hoto: Reuters

Wadanda suka shedar wa idanununsu sun ce 'yan kishin Islama sama da 60 sun mutu a cikin luguden wutan da sojojin na Faransa suka yi a garin Gao. Ita kuma gwamnatin Jamus tana ba da taimako ga sojojin na Faransa. Akan hakan akan ne ministan tsaron Jamus, Thomas de Maiziere ya fada a cikin firar da gidan rediyon ya yi da shi cewa Faransa ita ce kadai kasar da ta shiga Mali domin murkushe kokarin da 'yan tawaye ke yi na kwace iko da kudancin kasar. Ministan ya kara da cewa ko da yake Jamus ba za ta shiga yakin da ake yi da 'yan tawayen ba, to amma za ta ba da taimakon kayan aiki. A yau Litinin ne komitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya zai duba bukatar da Faransa ta mika game da halin da ke wakana a kasar ta Mali.

Mawallafiya: Halima Balaraba Abbas
Edita: Yahouza Sadissou Madobi