1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojoji sun kashe 'yan gudun hijira a Kwango

Abdul-raheem Hassan
September 16, 2017

Akalla 'yan gudun hijira 36 ne suka mutu, a yayin wani fito na fito tsakanin jami'an tsaro da masu zanga-zanga a kasar Kwango biyo bayan tirtsasa wasu barin kasar.

https://p.dw.com/p/2k7AQ
DR Kongo Bevölkerung in Goma nach den Angriff der Hutu Rebellen
Hoto: Getty Images/AFP/K. Maliro

Lamarin ya faru ne a yayinda 'yan gudun hijira da masu neman mafakar siyasa a kasar Kwango, ke bore kan yadda ake tilastawa wasu 'yan uwansu ficewa daga kasar. Jakadan Majalisar Dinkin Duniya da ke aikin tabbatar da zaman lafiya a kasar, ya ce akwai mutane 117 da hatsanioyar ya jikkata sannan an kashe guda daga cikin jami'an tsaron kasar.

A yanzu dai tuni jiragen masu saukar ungulu suka wuce da 'yan gudun hijira da suka samu munanan raunuka zuwa asibiti. Amma babu wani karin bayani daga bangaren rundunar sojin kasar, sai dai gwamnati ta umarci gudanar da bincike kan al'amarin.