Gomman mutane sun mutu a harin Ethiopiya
June 24, 2021Talla
Mai magana da yawun rundunar sojin, Kanar Getnet Adane, ya fada wa taron manema labaru cewar, an yi niyyar kai wa 'yan tawaye hari ne amma amma ba fararen hula ba, sabanin yadda ake yayatawa.
Ya kara da cewar, somamen da suka kai a garin Togoga na da nufin tarwatsa mayakan da ke mubayi'a ga hambararriyar jam'iyyar da ke mulki a Tigray, tare da gargadin cewar mayakan na fakewa ne da fararen hula.
Rahotanni na nuni da cewar akwai gomman mutane da ke kwance a asibitoci, wadansunsu sun rasa bangarorin jikinsu, a yayin da wasu ke jinyar munanan raunukan kuna, biyo bayan harin da rahotanni ke nuni da cewar yayi sanadiyyar rayukan sama da mutane 50.