1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Siriya: Ana kai sababbin hare-hare kan IS

November 12, 2017

Gwamantin Siriya ta tsananta kai hare-hare a yankin al-Bu Kamal sa'o'i kalilan bayan kwace iko da wasu muhimman garuruwa da mayakan kungiyar IS suka yi a kan iyakar kasar da Iraki.

https://p.dw.com/p/2nU7g
Syrien Kinder und Lehrern bei Luftangriff getötet
Hoto: picture-alliance/AP Photo/Revolutionary Forces of Syria

 Rahotanni sun ce hare-haren sun yi sanadin mutuwa tare da jikkata fararen hula masu yawa sakamakon luguden wuta ta sama da aka kwana ana yi. Kungiyar kare hakkin dan Adam da ke sanya idanu a yakin na Siriya wadda kuma ke da cibiya a Birtaniya, ta ce ana can ana ci gaba da musayar wuta tsakanin dakarun hadin gwiwa da kuma bangaren mayakan na IS a yankunan da ke kusa da yankin na al Bu Kamal. A ranar Alhamis ne dai kungiyar ta IS ta sake kwace gabashin lardin Dier al Zour mai arzikin man fetur.