Ko Alassane Ouattara za yi takara a zaben 2020?
June 2, 2018Talla
Hakan kuwa na faruwa ne a dai dai lokacin da ake fadi tashin ganin wanda zai gaje shi a matsayin na shugaban kasa an tabbatar da shi. A cikin wata hira da jaridar Jeune Afrique ta yi da shugaban na Cote d'Ivoire ya ce sabon kudin tsarin mulkin kasar ya ba shi damar yin takara daga shekara ta 2020. Sai dai kuma magoya bayan jam'iyyar PDCI na ganin cewar a shekara ta 2020 yakamata a ce shugaban kasa ya fito daga banganransu.