1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban Amirka ya yi jawabi a kungiyar Tarayyar Afirka

Suleiman BabayoJuly 28, 2015

Shugaba Obama na Amirka ya nemi tashi tsaye domin kawo karshen matsalolin cin hanci da rikice-rikice wadanda suka hana nahiyar Afirka bunkasa

https://p.dw.com/p/1G5nc
Äthiopien Addis Abeba Obama Rede Afrikanische Union
Hoto: Reuters/J. Ernst

Shugaba barack Obama na kasar Amirka ya gabatar da jawabi a helkwatar kungiyar Tarayyar Afirka da ke birnin Addis Ababa na kasar Habasha cikin ziyarar mataki na biyu na kasashen nahiyar. A cikin jawabi Obama ya nemi kasashen Afirka su tashi tsaye wajen kawar da cin hanci da rashawa da suka yi wa nahiyar katutu tare da dakile duk wani ci-gaba da ake bukata. Sannan ya nemi ganin ci gaba da yaki da ta'addanci da shawo kan rikice-rikice da ake samu a wasu kasashen nahiyar.

Shugaba Obama bayan nuna alfahari da kasarsa da yake jagoranta ta Amirka ya kara da cewa:

"Na kuma tsaya a gaban ku a matsayin dan Afirka. Afirka da mutanenta sun taimaka wajen bunkasar Amirka da mayar da ita babbar kasa a duniya, kuma Afirka ta mutanenta sun taimaka wajen inganta lamuran duniya."

Shugaba Barack Obama ya zama shugaban Amirka na farko da ya yi jawabi a helkwatar kungiyar ta Tarayyar Afirka da ke birnin Addis Ababa na kasar Habasha.