A cikin shirin za a ji cewar 'yan gudun hijira wadanda suka kauracewa rikicin 'yan Ambazoniya a Kamaru na fama da yunwa a cikin sansanonin da aka tsugunar da su a Najeriya. A kasar Ghana sakamakon yadda manyan jami'an gwamnati ke yin amfani da jiniya don kaucewa cinkoso ababen hawa, jama'a a kan tituna sun fara yin koyi.