A cikin shirin bayan labaran duniya akwai rahoto kan yadda dakarun sojin Ghana suka yi atisayen kakkabe ‘yan ta’addan da ke iyakarsu da Burkina Faso. Muna dauke da tattaunawa kan caccakar da masu sharhi ke yi wa gwamnatin Shugaba Buhari na Najeriya kan fara yunkurin tattaunawa da ‘yan awaren IPOB. Sai kuma rahoto kan jimamin da ake yi na mutuwar Mai Marataba Sarkin Katsinan Maradi a Nijar.