A cikin shirin bayan labaran duniya akwai rahoto kan zargin da kungiyoyin mata a Nijar suka yi wa sabuwar gwamnatin kasar na saba doka wurin nada ministoci sannan akwai bayani kan bukatar Gidauniyar Heinrich Böll ta kasar Jamus ta a yafe wa Najeriya basukan da ake bin ta. Akwai rahoto kan matashi a Kano da ya kirkiro injin wanki da rahoto kan sasanta al'ummomin kasar Libya.