Muna amfani da "Cookies" domin inganta abubuwan da muke wallafawa a intanet. Za ku iya samun karin bayani a kundin kare bayananmu.
A cikin shirin za aji cewa a karo na shida a cikin shekaru 35 shugaban Yuganda ya lashe zaben shugaban kasa, a Najeriya kuwa an kammala zabukan kananan hukumomin jihar Kano 44 wanda jamiyyar APC mai mulki ta lashe zaben.
Tura sakon Facebook Twitter Whatsapp Web EMail Facebook Messenger Web
Permalink https://p.dw.com/p/3o1nL
Kasashen duniya na zargin shugaban kasar Yuganda Yoweri Museveni ta take hakkin dan Adam. Wannan dai na zuwa ne bayan da rahotanni ke cewa har yanzu madugun adawar kasar Bobi Wine na karkashin daurin talala.
Gwamnatin tarayar Najeriya ta sanar da karin bude wasu iyakokin ta da sauran kasashe makobta wanda aka kwashe sama da shekara daya suna rufe. Hakan ya janyo martanin daga bangarori dabam-dabam a Nijar da Najeriya.
Jami'an tsaro a jihar Katsina da ke yankin Arewa maso Yammacin Najeriya, sun kubutar da wasu mutane tara 'yan Jamhuriyar Nijar da 'yan bindiga suka sato daga garuruwansu suka kai su jihar ta Katsina sukai garkuwa da su.
Dan damben boxing na Najeriya Kamaru Usman ya kafa tarihi, bayan da ya yi wasa 13 na duniya a jere ba tare da samun koma baya ko da sau guda ba.