Cikin shirin za a ji hukumar kula da harkokin sadarwa a Najeriya, ta fara binciken miliyoyin layukan wayoyin hannu daidai lokacin da matsalar sace-sacen mutane ke kara muni a kasar. A Nijar kuwa hukumomi ne ke daukar matakan rage farashin kayan masarufi yayin da azumi ke kawo jiki.