A cikin shirin za a ji cewar Sakataren MDD Antonio Guterres ya yaba da yarjejeniyar da aka cimma tsakanin Rasha da Turkiyya na samar da yankin tudun mun tsira a birnin Idlib na kasar Siriya. Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta sauke shugaban hukumar leken asiri na cikin gida Hans-Georg Maasen daga mukaminsa.