1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Samamen kakkabe 'yan tarzoma a Jamus

Usman Shehu Usman
June 23, 2017

Hukumomi a kasar sun kaddamar da samame a wurare dayawa cikin da ke gabashin kasar domin zakulo kungiyoyin masu tsattsauran ra'ayi.

https://p.dw.com/p/2fHWr
Deutschland Thüringen Razzia in rechtsextremer Szene
Hoto: picture-alliance/dpa/S. Thomas

Dama dai jami'an tsaro sun dira ne a jihar Thuringen da ke gabashin kasar kasar ta Jamus, don murgushe wasu gungun masu tsattsauran ra'ayi da ke da sansanin horas da magoya bayansu. Kungiyar masu kyamar baki ne dai sukan kai farmaki kan 'yan sanda,  da baki masu neman mafaka kana da Yahudawa. Samamen da aka kai a yau Juma'a, ya samu hadin gwiwar 'yan sandan jiha da na tarayya, a wani kokarin da hukumomi ke yi na kakkabe irin wadannan kungiyoyi.