1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ashton Carter ya isa gabashin kasar Malasiya.

Kamaluddeen SaniNovember 5, 2015

Sakatare harkokin tsaron Amirka Ashton Carter ya isa gabashin kasar Malasiya a ranar Alhamis din nan akan hanyar sa ta isa kudancin ruwan China domin tattauna muhimman batutuwan da suka hada da tsaro a yankin.

https://p.dw.com/p/1H0No
USA Verteidigungsminister Ashton Carter
Hoto: picture-alliance/AP Photo/K. Wolf

Babban dai kudirin wannan ziyarar ta sa shine domin ya sake fayyace irin manufofin harkokin tsaro a yankin.

to amma masu fashin bakin al'amuran siyasr yankin naganin matakin na iya tunzura mahukuntan China ne a dai dai lokacin kasashen biyu suke sa'in sa kan al'amura da dama.

Kazalika a ranar larabar nan sai da Sakataren tsaron Amirkan ya halarci wani taron ministocin tsaron yankin Asiya da aka gudanar a Malasiya a inda suka tattauna akan yanayin ruwan kudancin China.