1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sakamakon zaben Togo

July 27, 2013

Jami'iyyar Shugaba Gnassingbe ta kama hanyar lashe zaben majalisar dokokin Togo

https://p.dw.com/p/19FBr
A woman casts her ballot at a polling station in Lome on July 25, 2013 during Togo's parliamentary elections delayed by months of protests, with the opposition seeking to weaken the ruling family's decades-long grip on power. The polls mark the latest step in the impoverished country's transition to democracy after Gnassingbe Eyadema's rule from 1967 to his death in 2005, when the military installed his son Faure Gnassingbe as president. Today's elections are the first legislative polls since 2007, when Gnassingbe's party won 50 of 81 seats. Ninety-one seats are decided this time. AFP PHOTO/PIUS UTOMI EKPEI (Photo credit should read PIUS UTOMI EKPEI/AFP/Getty Images)
Hoto: Getty Images/AFP/Pius Utomi Ekpei

Rahotanni na wucin gadi na zaben majalisar dokokin da aka gudanar ranar Alhamis din da ta gabata a kasar Togo na nuna cewa jam'iyyar da ke mulkin kasar ta shugaba Faure Gnassingbe na kan gaba da kashi sittin da shida cikin dari na kuri'un da aka kidaya.

To sai dai jam'iyyun adawa a kasar na cewar an tafka magudi kuma za su kalubalanci sakamakon zaben, da za a fidda a hukumance, amma masu sanya idanu na kungiyar kasashen yammacin Afirka ta ECOWAS sun ce zaben ya gudana ba tare da wani magudi ba,sai dai sun ce sun bankado wasu kurakurai nan da can.

Tuni dai jami'an ECOWAS da aka gudanar da zaben na Togo kan idonsu suka yi kira ga al'ummar kasar da su guji ta da hankali gabanin fitar sakamakon zaben na din-din-din inda suka kara da cewar kyautuwa ya yi masu korafi game da zaben su ruga kotu maimakon daukar doka a hannunsu.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita. Halima Balaraba Abbas