1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sace jami'an wanzar da zaman lafiya

August 28, 2014

tsagerun da ke yaƙar gwamnatin Siriya sun sace jami'an wanzar da zaman lafiya na Majalisar Ɗinkin Duniya.

https://p.dw.com/p/1D3KX
Hoto: AFP/Getty Images

Rahotanni da ga ƙasar Siriya na nuni da cewar tsagerun da ke yaƙar gwamnatin ƙasar sun sace wasu ma'aikatan wanzar da zaman lafiya na Majalisar Ɗinkin Duniya a Tuddan Golan da ke ƙarƙashin mamayar Isra'ila. Wani jami'in Majalisar ta Ɗinkin Duniya da ya nemi a sakaya sunansa ya sanarwa da kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa ma'aiakatan Majalisar 43 ne aka sace.

Mawallafiya: Lateefa Mustapha Ja'afar
Edita: Abdourahamane Hassane