1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ranar wadanda rikicin addini ya shafa

Lateefa Mustapha Ja'afar
May 29, 2019

Babban zauren Majalisar Dinkin Duniya, ya amince da wani kudiri da ya ware ranar 22 ga watan Agusta na kowacce shekara ta zamo ranar tunawa da wadanda rikicin addini da fahimta ko kabilanci ya rutsa da su.

https://p.dw.com/p/3JNjD
UN-Vollversammlung verurteilt Israel für Gewalt im Gazastreifen
Babban zauren Majalisar Dinkin DuniyaHoto: picture-alliance/Xinhua/Li Muzi

Baki dayan mambobin babban zauren Majalisar ta Dinkin Duniya 193 dai, sun amince da wannan kudiri da kasashen Brazil da Masar da Iraki da Jordan da Najeriya da Pakistan da Poland da kuma Amirka suka gabatar. Yayin kaddamar da kudirin, sun nuna matukar damuwarsu kan matsalar rashin martaba ra'ayin juna da kuma tashe-tashen hankula da ke faruwa tsakanin mabiya addinai da ma masu banbamcin fahimta cikin addini ko kuma al'umma guda, inda suka jaddada cewa babu wata alaka tsakanin duk wani aiki na tsattsauran ra'ayi ko ta'addanci da kowanne addni ko kasa ko kuma kabila.