1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabon firaministan Yemen ya yi marabus

Al Amin Suleiman MohammedOctober 9, 2014

Ahmed Awad Ben Mubarak ya ce ya ajiye aikin ne domin samun haɗin kan ƙasar.

https://p.dw.com/p/1DSNd
Jemen designierter neuer Regierungschef Ahmed Awad bin Mubarak
Hoto: Reuters/Khaled Abdullah

Marabus ɗin na firaminista na da nasaba ne da ƙin amncewa da 'yan tawayen na 'yan Shi'a waɗanda ke da iko da birnin Sana'a tun cikin watan Satumba suka ƙi amincewa da naɗin.

A cikin wata wasiƙa da ya aikewa shugaba Abd Rabo Mansur Hadi,firaminista ya ce ya ɗauki wannan mataki ne domin kaucewar rabuwar kasar gida biyu. A cikin watan jiya ne aka cimma wata yarjejeniya dakatar da buɗe wuta tsakanin gwamnatin da 'yan tawayen a ƙarƙashin jagorancin Majalisar Ɗinkin Duniya tare da kafa gwamatin haɗin kansa.