Rwanda: Shugaba Kagame ya yi hasashen nasara
August 1, 2017Talla
Cikin wannan mako ne dai aka tsara yin zaben shugaban kasa a kasar wadda ke zama cikin kananan kasashen yankin gabashin Afirka. Mr. Kagame wanda ke mulkin kasar shekaru 17 a yanzu, ya yi nasarar samun tsayawa takara karo na uku ne bayan sauya tsarin mulkin kasar a shekara ta 2015, a zaben raba gardamar da kasashen duniya suka aza ayar tambaya a kansa.
Ana dai kallon ta yiwu shugaban na Ruwanda mai shekaru 58 na iya zama bisa karaga kar i zuwa shekara ta 2034, shubanan da aka yaba wa kokarin kyautata al'amuran kasar bayan kisan kiyashin da ya halaka kimanin mutane miliyan guda cikin shekara ta 1994.