1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rundunar tsaro ta JTF ta kame wasu yan ƙungiyar boko haram a Najeriya.

March 3, 2013

Rundunar ta tabbatar da tsaro da zaman lafiya a jihar Borno da ke a yankin arewacin Tarrayar Najeriya, ta ce ta kashe wasu data bayyana ‘yan kungiyar Boko haram su guda 20.

https://p.dw.com/p/17pa0
Soldier patrol to monitor protesters at Ojota district in Lagos on January 16, 2012. Nigerian security forces fired tear gas and shot into the air Monday to disperse around 300 protesters in Lagos as authorities moved to prevent demonstrations in various parts of the country. Nigerian unions announced on January 16 they were suspending a week-old nationwide strike over fuel prices which has shut down Africa's most populous nation and brought tens of thousands out in protest. AFP PHOTO/PIUS UTOMI EKPEI (Photo credit should read PIUS UTOMI EKPEI/AFP/Getty Images)
Hoto: Getty Images/AFP

Rundunar ta ce ta kashe yan' bindigar ne bayan wani hari da dakarunta suka kai a barakin Sojoji da ke Mongunu ,da ke da nisan Kilomita 200 daga Maiduguri kan iyaka tsakanin Cadi da Kamaru.

Kakakin rundunar laftanar kanar Sagir Musa ya shaidawa manema labarai cewar sun samu nasarar gano wasu muggan makamai da abbaban hawa da aka nufi kai wannan harin da su, wanda bai sami nasara ba.Haka kuma rundunar ta ce ta kame wasu jigajigan ‘kungiyar da suka kitsa kai hari Maiduguri bayan kammala taron gwamnonin.

Mawallafi: Abdourahamane Hassane
Edita : Umaru Aliyu.