1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kokarin murkushe masu adawa da tazarce a Burundi

Gazali Abdou Tasawa/LMJApril 27, 2015

Hukumomin kasar Burundi sun dauki matakin rufe wani gidan radio mai zaman kansa a kasar bisa zargin tunzura al’umma ga bijirewa dokokin gwamnati.

https://p.dw.com/p/1FFrb
Kokarin tarwatsa masu zanga-zanga a Burundi
Kokarin tarwatsa masu zanga-zanga a BurundiHoto: Reuters/T. Mukoya

Rahotanni sun bayyana cewa tuni aka kwace lasisin izinin aiki na wannan gidan Radiyo inda a gefe guda kuma hukumomin suka soma farautar wasu shugabannin kungiyoyin farar hula. An dai cafke shugaban hadaddiyar kungiyar kare hakkin dan Adam ta kasar Pierre-Claver Nmbonimpa tare da bada sammacin kamo Vital Nshimirimana jagoran kungiyoyin farar hula bisa kaddamar da wani kampe na nuna adawa ga shugaba Nkurinziza. Majalisar Dinkin Duniya ta kiyasta cewa kimanin 'yan kasar ta Burundi 15,000 ne suka tsere zuwa makwabciyarta Ruwanda domin tsira da rayukansu daga barazanar kisa da kungiyar 'yan bangar siyasa ta Nmbonerakure da ke goyan bayan tazarcen na Shugaba Nkurinziza ke yi musu.