1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rudani kan siyasar kasar Burkina Faso

Abdourahamane HassaneNovember 7, 2014

Babu tabbas a kasar Burkina Faso a game da wadanda za su jagoranci gwamnatin wucin gadi ta kasar, bayan faduwar gwamnatin Blaise Compaore

https://p.dw.com/p/1DjAM
Burkina Faso Zida mit Oppositionsanführer Diabre 02.11.2014
Hoto: Reuters/J. Penney

Har kawo yanzu babu tabbas a kasar Burkina Faso a game da wadanda za su jagorancin gwamnatin wucin gadi ta kasar, bayan faduwar gwamnatin Blaise Comapore a makonni da suka gabata, duk kuwa da gargadin da kungiyar Tarrayar Afirka ta yi ga shugaban gwamnatin mulkin soji Lt Kanar Yacouba Isaac Zida cewar ya mika mulkin ga farar hula a cikin makonnin da ke tafe, da alama an shiga rudani a kasar na sabanin da ke tsakanin 'yan siyasar da kungiyoyin fararen hula a kan batun kafa gamnatin rikon kwaryar.

Kalubalen da 'yan siyasa da kungiyoyin fararen hula a Burkina Faso suke fuskanta a kan maganar kafa gwamnatin rikon karya, wanda tun kafin yin boran da ya share gwamnatin ta Blaise Compaore 'yan siyasar ba su tsara makomar gwamnatin wucin gadin da kuma yadda za ta kasance, kamar yadda Koffi Amétépé, editan wata mujallar a kasar ta Burkina Faso ya bayyana.

Militärputsch in Bukina Faso 01.11.2014
Hoto: picture-alliance/dpa/Etienne Kafando

Sai dai cewar wani kwamiti da aka girka wanda ya hada wakilan 'yan siyasa da kungiyoyin farar hula da kuma sarakuna gargajiya na tattauna wani tsari na yadda gwamnatin rikon kwarya za ta kasance da kuma mutanen da suka cancanta a zaba.

Duk da haka akwai jan kafa a cikin lamarin wanda wasu suke tunani cewar a maimakon a wakilta 'yan siyasa ko wakilan kungiyar farar hula abin da ya fi shi ne a mika jagorncin gwamnatin ga shugabannin addinai.

Miliär übernimmt Staatsfernsehen in Bukina Faso 02.11.2014
Hoto: Issouf Sanogo/AFP/Getty Images

Desire Boniface wani mai limanci a jami'ar birnin Wagadugu ya ce dama 'yan majami'ar Katolika sun taba rike wani matsayi a baya na aikin gwamnatin na bincike.