1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin Siyasar Bangladesh ya yi ƙamari

November 9, 2013

A ƙasar Bangladesh 'yan adawa na fuskantar barazana daga ɓangaren gwamnati wacce ke naman murƙushesu da ƙarfin tuwo.

https://p.dw.com/p/1AEd8
Hoto: Reuters

Hukumomi a ƙasar ta Bangladesh sun cafke shugabannin babbar jam'iyyar adawar ƙasar su guda uku gabannin babban zaɓen ƙasar da za a gudanar a shekara mai zuwa.

Jami'an 'yan sanda sun cafke Moudud Ahmed da M.K Anwar da kuma Rafiqul Islam Mia na jam'iyyar adawar a jiya Jumma'a, sa'oi ƙalilan bayan da haɗakar ma'aikatan ƙungiyar ƙwadago ƙarkashin jagorancin jam'iyyar adawa ta Bangladesh Nationalist Party, suka sanar da fara yajin aikin a gobe Lahadi. Rahotanni sun bayyana cewar yajin aikin na kwanaki uku, an shirya yin sa ne domin tilastawa Firaministan ƙasar Sheikh Hasina sauka daga kan karagar mulki tare da naɗa wani shugaban na wucin gadi da zai lura da al'amuran zaɓen da za a gudanar a ƙasar.

Mawallafiya: Lateefa Mustapha Ja'afar
Edita: Abdorahamane Hassane