1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin siyasa a DRC

May 29, 2007
https://p.dw.com/p/BuKQ

A wani saban bori na siyasa, a Jamhuriya Demokraɗiyar Kongo, yan Majalisar dokokin yankin Kivu, sun ƙauracewa Majalisar.

Sun gita sharaɗin komawa kan kujerun su ,da tabbatar da tsaro a yankin Kivu, da ke fama da yaƙe- yaƙe.

Yan majalisar sun zargi gwamnatin Joseph kabila, da rashin taɓuka komai, ta fannin magance matsalolin tsaro a Kivu.

A watan da ya gabata, hukumar Majalisar Ɗinkin Dunia mai kulla da kare yancin bil Adama,ta ja hankalin gwamnatin Kinshasa, a game da cin zarafin yaya mata, a wannan yanki.