Rikicin siyasa a DRC
May 29, 2007Talla
A wani saban bori na siyasa, a Jamhuriya Demokraɗiyar Kongo, yan Majalisar dokokin yankin Kivu, sun ƙauracewa Majalisar.
Sun gita sharaɗin komawa kan kujerun su ,da tabbatar da tsaro a yankin Kivu, da ke fama da yaƙe- yaƙe.
Yan majalisar sun zargi gwamnatin Joseph kabila, da rashin taɓuka komai, ta fannin magance matsalolin tsaro a Kivu.
A watan da ya gabata, hukumar Majalisar Ɗinkin Dunia mai kulla da kare yancin bil Adama,ta ja hankalin gwamnatin Kinshasa, a game da cin zarafin yaya mata, a wannan yanki.