Baki na son kauracewa Afirka ta Kudu
October 10, 2019Talla
Sama da masu neman mafaka 250 a Afirka ta Kudu na neman hukumomi su gaggauta fitardasu daga kasar saboda rashin tsaro. Matakin da bakin suka dauka na da nasaba da munanan hare-hare kin jinin baki da ya faru watanni da suka gabata.
Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD a kasar ba su yi martani kan wannan sabuwar dambarwa ba tukuna. Kasashen Afirka da dama ciki har da Najeriya sun yi Allah wadai da yadda aka yi ta kashe baki da lalata dukiyarsu a Afirka ta Kudu.