1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rasha za ta sasanta Amirka da Koriya ta Arewa

Zulaiha Abubakar MNA
December 26, 2017

Bayan tsamin dangantakar da ke tsakanin Shugaba Kim Jong-Un da Donald Trump, kasar Rasha na fatan shiga tsakanin bangarorin biyu da nufin kawo karshen takaddamar da ke tsakaninsu.

https://p.dw.com/p/2pxTN
Kombi-Bild  Trump und Kim Jong Un
Hoto: Reuters/K. Lamarque/KCNA

Gwamnatin kasar Rasha ta sanar cewa tana yunkurin sulhunta tsamin dangantakar da ke tsakanin kasashen Amirka da Koriya ta Arewa, in har bangarorin biyu sun amince da wannan tayin.

Ministan harkokin wajen kasar Sergei Lavrov ya yi kira ga kasashen biyu da su hau teburin sulhu bayan kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya amince da kakaba wa kasar ta Koriya ta Arewa takunkumi a makon da ya gabata, sakamakon gwajin makaman kare dangi da kasar ke ci gaba da yi wanda ke zama barazana ga duniya baki daya.