1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jam'iyyar PJD ta sha kaye a zaben Maroko

Abdoulaye Mamane Amadou
September 9, 2021

A karon farko jam'iyyar PJD ta masu matsakaicin kishin addini da ke mulkin Maroko, ta sha mummunan kaye a zaben 'yan majalisun dokokin kasar da aka gudanar, inda ta samu kujeru 12 kawai.

https://p.dw.com/p/406KB
Marokko | Wahlen
Hoto: Abdelhak Balhaki/REUTERS

Gungun jam'iyyun 'yan adawa ne dai suka kifar da jam'iyyar a yayin zaben kasar da aka yi a jiya, bayan da suka lashe kujeru mafi rinjaye na 'yan majalisun dokokin Marokon kasar 395, a yayin da jam'iyyar PJD ta samu kujeru 12 kawai, lamarin da ya takaita burinta na karin wa'adi na uku a kan madafan iko.

A yanzu Sarki Mohammed na VI ne ke da hurumin nada daya daga cikin jiga-jigan jam'iyyun da suka yi rinjaye a matsayin sabon shugaban gwamnati, kana kuma ya gayyaci jam'iyyun da su gabatar da wani sabobon tsari na raya kasa da zai dace da sabbin manufofin sarkin na sauye-sauye a kasar.