1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Paris: Wani mutum ya kaiwa 'yan sanda hari

Nura Datti KankarofiJanuary 7, 2016

'Yan sandan Faransa sun harbe wani mutum har lahira bayan da ya tinkari wani caji ofis dazu sanye da riga ta kunar bakin wake da kuma wuka a hannunsa.

https://p.dw.com/p/1HZo1
Frankreich Polizei erschießt Mann vor Pariser Kommissariat
Hoto: Getty Images/AFP/L. Bonaventure

Wani mutum da ya shaida faruwar lamarin wanda ya auku a birnin Paris ya ce mutumin ya yi ta kabbara da babbar murya lokacin da ya doshi ofishin 'yan sandan, sai dai bayan da aka hallaka shi an gano cewar rigar kunar bakin waken ta jabu ce.

Tuni dai aka jibge jami'an tsaro da kuma kwararru da ke kwance abubuwa masu fashewa a inda abin ya faru. Yanzu haka dai kwararrun na can suna cigaba da gudanar da bincike. Ya zuwa yanzu ba a kai ga bayyana sunan wannan mutumi ko ma kasar da ya fito ba.

Lamarin dai na zuwa ne jim kadan bayan kammala jawabin Shugaba Francois Hollande, shekara guda bayan da aka kai hari kan gidan jaridar nan ta Charlie Hebdo da ke zane-zanen barkwanci.