1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus: Ana binciken masu alaka da maharin Vienna

Abdul-raheem Hassan
November 6, 2020

Gwamnatin Ostiriya ta umarci rufe wani masallaci na masu tsatsauran ra'ayi a kasar, bayan wani harin ta'addanci da ya kashe mutane a binrin Vienna.

https://p.dw.com/p/3kxbm
Österreich Wien nach dem Terroranschlag
Hoto: Matthias Schrader/AP Photo/picture alliance

Jami'an 'yan sandan Jamus sun kai samame gidaje da wuraren kasuwancin wasu mutane hudu, da ake zargin suna da alaka da maharin ta'addancin da ya halaka mutane a birnin Vienna.

Bayan gudanar da buincike kan mutanen a biranen Osnabruek da Kassel da kuma Pinnerberg, 'yan sandan sun ce ba a tuhumar mutanen kai tsaye da harin, amma akwai shedu da ke nuna mutanen na da wata alaka da wanda ya kai harin.

Mutane biyar ne suka mutu a harin ta'addanci ciki har da maharin, wasu mutane 20 sun jikkata har da dan sanda. Kasashen duniya sun yi tir da harin tare da neman daukar matakan hana aukuwar haka nan gaba.