Nijar: 'Yan adawa sun ce PNDS ta karya doka
April 4, 2019Talla
Sanarwar mai dauke da sa hannun shugaban hadin gwiwar jam'iyyun siyasar na adawa na FRDDR, an yi ta ne da sunan ‘yan adawar kasar ta Nijar baki daya, inda suke neman da a sauke Mohamed Bazoum daga mukaminsa na ministan cikin gida bayan da aka nadashi dan takarar neman shugabancin kasa. 'Yan adawar sun ce ba daidai ba ne Bazoum din ya ci gaba da rike matsayin minista cikin gida bayan jam'iyyarsa ta bayyana takararsa a zaben shugaban kasa na shekara ta 2021.