1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

''Tarkama''saddabarun zakulo masu laifi

Mohammad Nasiru Awal AH
July 7, 2020

A Jamhuriyar Nijar har yanzu matsafa magadan gargajiya na rike da wata al'adar da ake kira ''Tarkama'' da ke tattare da mamaki da ke zakulo masu aikata barna daga cikin al'umma, batun da shirin Taba Ka Lashe ya duba.

https://p.dw.com/p/3etz0
Wannan wani tsohon hoto ne muka yi amfani da shi
Wannan wani tsohon hoto ne muka yi amfani da shiHoto: DW/E. Lafforgue

Duk da shigowar addinin Musulunci har yanzu magada al'adu na shirya a wasu sassan Nijar irin su Tahoua abubuwa na gargajiya na a'aldu. Daya daga cikin dadaddun gargajiya da ake ci gaba da raya su ita ce al'adar Tarkama da ake shiryawa a duk lokacin da wasu ko wani daga cikin al'umma ya aikata wani laifi kamar na maita. Tarkama ke nuna mai laifin a cikin bainar jama'a duk inda ya boye. Matsafi Shaibu shi ne shugaban matsafa na garin Dagarka da ke Konni na Jihar Tahoua, ya ce al'adar na yin tasiri a kan rayuwar al'umma ta yau da gobe. Kamar sauran sabgogi wannan sabgar ta Tarkama dai ba ta yiwuwa sai dai matasa majiya karfi wadanda ake amfani da su wajen tada Takarmar. Dubban mutane ne dai ke zuwa kallon al'adar a duk lokacin da ake yin ta.