1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bakin haure sun koma gida daga Libiya

Abdoulaye Mamane Amadou
July 20, 2019

Hukumomi a Jamhuriyar Nijar sun kaddamar da wani tsarin mayar da 'yan kasar bakin haure da masu ci rani a gida, bayan sun shafe lokaci suna tsare a cibiyoyin da ke tsare bakin haure a kasar Libiya.

https://p.dw.com/p/3MQaD
IOM bringt Flüchtlinge aus Libyen in Heimatländer zurück
Hoto: AFP/Getty Images/M. Turkia

Akalla 'yan ci rani 900 ne 'yan asalin Jamhuriyar Nijar da ake rike da su a cibiyoyin rike bakin haure a kasar Libiya suka koma gida, daga farkon watan Janairun wannan shekarar zuwa yanzu kamar yadda wata majiya daga hukumar kula da kaurar jama'a ta MDD IOM ko OIM ta bayyana a yau din nan.

Ko a ranar Juma'ar nan wani jirgin shake da yan ci rani daga kasar ta Libiya ya sauka a birnin Niamey dauke da bakin haure  147  ciki har da wasu kananan yara tara.

Kamfanin dillancin labarai na Faransa AFP ya ruwaito cewa galibin wadanda aka dawo da sun daga Libiya 'yan asalin yakin Tahoua ne a yammacin kasar, da kuma na yankin Zinder da ke tsakiya maso kudanncin Jamhuriyar ta Nijar din wadanda dukkaninsu suka jima a hannun jami'ai da ke kula da cibiyoyin tare jama'a bakin haure da 'yan ci rani a kasar Libiya.