1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar: An halaka 'yan ta'adda 15 kan iyaka da Mali

Gazali Abdou Tasawa
December 30, 2018

A Jamhuriyar Nijar, sojojin gwamnati hadin gwiwa da na kasar Faransa mambobin rundunar tsaron ta Barkhane sun yi nasarar halaka mayakan kungiyoyin 'yan ta'adda masu da'awar jihadi guda 15 a kan iyaka da kasar Mali. 

https://p.dw.com/p/3An6j
Soldaten im Niger
Hoto: Desmazes/AFP/Getty Images

Ministan tsaron kasar ta Nijar ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwar da ya fitar a wannan Asabar inda ya ce sojin kasa na kasashen biyu a bisa rakiyar jiragen helikofta da na yaki ne suka kai farmakin a yankin Arewa maso yammacin kauyen Tongo-Tongo na jihar Tillaberi inda sojojin Nijar biyar da na Amirka hudu suka halaka a cikin wani harin da 'yan ta'addan suka kai masu a watan Oktoban 2017. 

A yayin farmakin sojojin kasashen biyu na Nijar da Faransa sun yi nasarar kwace wurare da dama na fakewar 'yan ta'addan tare da karbo baburra kimanin 20 da bindigogi 26 da tarin harsasai. Sanarwar ta ce ba a samu asarar ray ko daya ba daga bangare sojojin kasashen biyu a cikin wannan farmakin wanda sojojin suka kai a cikin daren Alhamis washe garin Juma'ar da ta gata.