1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Netanyahu ya kaurace wa minista Gabriel..

April 25, 2017

A wani abu da ke nuna alamar kara tsamin dangantaka tsakanin Israila da Jamus, Firaministan Israila Benjamin Netanyahu ya soke ganawa da ministan harkokin wajen Jamus Sigmar gabriel a Irsraila..

https://p.dw.com/p/2buy0
Ministan harkokin wajen Jamus Sigmar Gabriel a dama tare da Dormitio-Abtei dan kungiyar farar hula mai adawa manufofin Israila a yankin Falasdinawa.
Ministan harkokin wajen Jamus Sigmar Gabriel a dama tare da Dormitio-Abtei dan kungiyar farar hula mai adawa manufofin Israila a yankin FalasdinawaHoto: picture-alliance/dpa/B. von Jutrczenka

Firaminmistan Israila Benjamin Netanyahu ya soke ganawar da aka shirya a ranar Talatar nan tsakaninsa da Ministan harkokin wajen Jamus Sigmar Gabriel bayan da ministan na Jamus da ke ziyara a Israila ya tattauna da wasu kungiyoyi masu adawa da mamayar da Israila ta yiwa wasu yankunan Falasdinawa.

Wannan takaddamar da ta kunno kai dai na neman fadada rashin jituwa tsakanin Israilar da Jamus kan batun Falasdinawa.

Jamus dai na kara yin kakkausar suka ga manufofin gwamnatin Israila ta Benjamin Netanyahu na fadada matsgunai a yankunan da Falasdinawa ke son kafa kasarsu.

Yayin da ya kai ziyara birnin Ramallah a yankin gabar yamma, ministan harkokin wajen jamus Sigmar Gabriel ya gana da Firaministan Falasdinawa Rami Hamdallah, inda shugabannin biyu suka gudanar da taron manema labarai na hadin gwiwa.